Skip to main content

Posts

Showing posts from May, 2019

DAN ZARIA A RESTAURANT

Wani shakiyin Bazazzagi ne ya yi dinkinsa babbar riga mai asake akan wata dalleliyar shadda ruwan kwai. Da ka ganshi ka ga mai hannu da shuni. Ai kuwa sai ya nufi gidan abinci (Restaurant), ya samu waje ya zauna ya kwalawa mai restaurant kira da karfi ya ce “Hado min plate na Naira 2,000 kuma ki hadawa kowa da ke wajen nan plate na Naira 3, 000 saboda idan ina cin abinci, ina so naga kowa yana ci”. Duk mutanen da ke wajen suka fara godiya yayin da mai restaurant ta zubawa kowa nasa ta kawo masa hadin girma. Shinkafa da dankalin turawa da farfesun kayan ciki ko kifi ko naman kai, ya dai danganta da abinda mutum ke so. Kana ga hadin kwadon kayan lambu da a turance a ke kira da salad Bayan mutumin ya gama cin abinci sai ya kuma cewa mai abincin “kawo min abin sha na Naira 500 kuma ki baiwa kowa na Naira 1, 000 saboda idan ina shan abu, ina so naga kowa yana sha”. Mai Restaurant ta kaiwa kowa kayan shaye-shaye kala-kala. Nan fa mutanen wajen suka barke da shewar “Allah ya kiyaye ka!” Bayan...

YADDA AKE SADUWA DA MAI CIKI

Tambaya : Malam na kan ji wasu mutane na fadar cewa ba ya halatta idan matar mutum tana da juna biyu ya yi jima'i da ita har sai ta haihu meye gaskiyar maganar ???????? AMSA : To dan'uwa ya halatta a sadu damace lokacin da take da ciki, saboda fadin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi : "Duk wanda ya yi imani da Allah da ranar lahira, to kada ya shayar da ruwansa ga shukar waninsa" Abu-dawud : 1847 Ibnul kayim yana cewa :"Wannan hadisi yana nuna cewa ciki yana kara karfi duk lokacin da ake saduwa, saboda Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kamanta shi da shuka, ita kuma shuka tana kara girma, idan aka ba ta ruwa" Tahzibussunan 1\193 . Masana likitanci suna cewa: Ba'a so miji ya dinga hawa kan matarsa lokacin da take da ciki, zai fi kyau ta dinga yin goho yayin da za su sadu, ko kuma ya sadu da ita ta gefe, saboda kwanciya akanta yana iya wahalar da yaron . Sannan yawanci mata ba su cika son yawan saduwa ba idan cikinsu ...
MAGANIN CIWON HAKORI Ciwon hakori ciwo ne dake yawan addaban al'uma musamman a lokacin sanyi ga duk mai wannan larura insha Allahu zaka samu waraka idan kayi amfani da wannan hanyan: A samu dakakken kanimfari sai ahaɗashi da man kwakwa a gauraya sai asamu wani siririn kwalba azuba aciki kamar yadda ake gani sannan daga bisani aɗiga akan hakorin inda yake ciwo, za a maimaita hakan safe dayamma, da iznin Allah za arabu da matsalan ciwon hakori. Zaku samu magunguna masu kyau a shagonmu na haske Islamic chemist dake kawo market gaban masallacin Yenmasara kawo kaduna Domin Karin bayani a turo sako ta whatsapp 08037624598

ALAMOMIN DA ZAKA GANE MACE BATA SON KA

Wasu daga cikin alamomin da zasu tai makama kagane budurwa bata sonka. : 1~ zakaga sautari kana hira da ita bata sakewa tayi hira, sai dai kaji tana um, eh, a a, to, to ya zance ma, kuma bawai rana daya ba, bakuma laifi kaimata ba, kuma kasan ita me surutuce bawai kunyaceba a a ranaku dayawa inkuna zance haka take yima. : 2~ wata zata dinga yawan tunani, alokacin da kuke hira inkai magana tace ina ji ba kace kaza da kaza ba ta dan fadi 2/5 na abun da kace tai shuru. : 3~ kallon raini a fakaice, ko a dan fake ka a harareka : 4~ Inkatura a kirata bata fitowa dawuri kuma ba ace ma tana wani abunba kamar cin abunci wanka, kwalliya da sauransu, kuma intazo bakaga alamar sabuwar kwalliya ba, kuma batace ma, masoyi kayi haquri na batama lkc, kaza da ka nakeyi. kuma kullun hakatake ma. : 5~ Bata fiyayin kwalliya in kazo ko a yaya ta fito, watama saita munanta kanta zata fito dan kace baka so : 6~ In matan gidansu ko qawayenta suna hirarka suna fadar kirkinka ita zata dinga jin haushi, kota tas...

MAGANIN CIWON SANYI NA MAZA

Don girman Allah a taimaka a amsa man tambayata. Allah yaima sakayya da gidan Aljanna mlm. na kasance daya daga cikin members na wannan page kuma ina bibiyar fatawoyinka. mlm ina fama da matsalar sanyi (gonorrhoea), wato wani farin ruwa ke fitowa daga azzakarina shine nake so mlm ya taimaka man da magani don naji ance wannan matsalar na hana mutum haihuwa kuma gashi saura wata ukku bikina, sannan kuma ina gudun kar in gogama matar da xan aura. na jarraba wani daga cikin magugunan da kai bayani ga irin wannan mtslar a baya na garin tafarnuwa, citta da kustilhindi a cikin zuma duk inna sha sai zuciyata ta rika yin ciwo. kuma na jarraba wanda ka bada ga tambaya ta 1458 shima ban dace ba. mlm a taimaka a amsa man don na dade ina fama da wannan matsalar kuma abin na damuna. mlm a boye sunana. na gode. AMSA ******* Shi wannan sanyin gaskiya yana da wahalar jin magani. Domin kuwa wadancan abubuwan da ka ambata a baya, mutane da yawa sun jarraba kuma sun samu waraka da yardar Allah. Amma ga wa...

MAZAN ZAMANI

A wannan zamanin da muke ciki in kana neman kwararrun mayaudara wadanda sun kware kuma sun san salo iri-iri na yaudarar 'yan mata sune mazan wannan zamanin da muke ciki.sai yace hana son ta amma cikin zuciyar sa babu komai sai tsabagen yaudara da dabarun yadda zai sami nasara ya tsima ta don neman cin nasara a abin da ya hango kuma shi ya kai shi.shi fa ba auren ta zai yi ba amma saboda ya riga ya kafa mata tarko kuma yayi nasrar kama ta kurunkus, ta faru ta kare.a haka zai cigaba da cin nasara a kan ta daga gaya in ya gama cin moriyar ganga sai ya fasa ya canza sabuwa.ita kuma sai ta zama abar tausayi mai nadama da dana sani, da na sani keya ce.